Muhammadu Buhari
Kwamitin tsaro na kasa (NSC) karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin bude kamfanin siminti na Dangote da ke Obajana a jihar Kogi da gaggawa.
Majalisar ta bayar da umarnin ne a wani taro da ta gudanar a zauren majalisar dokokin jihar da ke Abuja.
Ministan harkokin ‘yan sanda, Mohammed Dingyadi, tare da takwaran sa , Rauf Aregbesola da babban hafsan tsaron kasa (CDS), Janar Lucky Irabor, sun bayyana wa manema labarai kadan daga cikin abinda aka tattauna a taron.
Aregbesola ya ce an cimma yarjejeniya tsakanin gwamnatin jihar Kogi da kamfanin Dangote kan bukatar sake bude masana’antar siminti, inda aka bukaci bangarorin biyu su sanya hannu a bisa yarjejeniyar.
Ministan ya kara da cewa majalisar ta ba da umarnin bude masana’antar da gaggawa tare da ba da shawarar cewa duk wasu batutuwan da ake takaddama a kai a war ware bisa tsarin doka, domin gwamnati ta himmatu wajen samar da ayyukan yi.
0 Tsokaci