Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato| Hoto Daga: RFI
Hajiya Hadiza, babbar jikar tsohon firaministan arewacin Najeriya kuma Sardaunan Sakkwato, Sir Ahmadu Bello, ta rasu.
Hajiya Hadiza ta rasu bayan gajeriyar jinya a jihar Sakkwato.
Marigayiyar 'ya ce ga Wamban Kano, Abubakar Dan Maje.
Haka kuma marigayiyar tsohuwar matar Shehu Kangiwa ce, tsohon gwannan Sakkwato.
Marigayiyar wacce aka haifa a shekarar 1960 ta rasu ta bar 'ya'ya uku.
Tuni aka sallace ta a gidan marigayi Firimiya da ke kan titin Diori Hammani dake Sakkwato.
0 Tsokaci